A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kwamishinan Matasa da Wasanni na Jihar Katsina, Injiniya Sirajo Yazid Abukur, ma’aikatar ta bayyana cewa labarin da ake yadawa cewa magoya bayan Katsina United sun tayar da tarzoma a lokacin wasan su da Barau FC ba gaskiya ba ne.
Ma’aikatar ta ce bayan cikakken bincike daga jami’an tsaro, jami’an wasan, da masu sa ido masu zaman kansu, babu wani abu da ya nuna an samu tashin hankali ko jikkata mutum. An tabbatar cewa wasan ya gudana cikin kwanciyar hankali, inda magoya baya daga ɓangarorin biyu suka nuna ladabi da girmamawa.
Sanarwar ta yaba da yadda ’yan wasan da magoya bayan Katsina United ke ci gaba da zama abin koyi wajen nuna halin kirki a filayen wasa, tare da jaddada cewa Jihar Katsina ta dade tana da suna wajen nuna ɗabi’a da biyayya a wasanni.
Ta kuma shawarci jama’a da su guji yada labaran ƙarya da jita-jita marasa tushe da ka iya tayar da hankali, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da kula da harkokin wasanni cikin zaman lafiya da tsaro ga kowa da kowa.



