DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku rungumi zaman lafiya a tsakaninku duk wanda muka kama zai fuskanci fushin hukuma – Gwamna Nasir Idris ga manoma da makiyaya

-

Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya gargadi manoma da makiyaya da ke rikici a karamar hukumar Arewa ta jihar su daina fada su zauna lafiya, inda ya ce duk wanda aka kama yana tayar da fitina za a kama shi a gurfanar da shi gaban kotu.

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara ga mutanen da suka rasa matsuguni sakamakon rikicin, wadanda ke samun mafaka a ofishin karamar hukumar da ke Kangiwa.

Google search engine

A cewarsa, yaje ne don jajanta wa iyalan wadanda suka mutu a wannan mummunan rikici, sai dai ya gargadi garesu da su daina daukar doka a hannu.

Gwamnan ya kuma ce ana nan ana gudanar da bincike,duk wanda aka kama da hannu kan wannan rikici tabbas zai fuskanci fushin hukuma tare da gurfanar da shi domin daukar mataki na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara