Sojojin Nijeriya sun kai farmaki kan ’yan ta’adda da masu aikata laifuka a faɗin Nijeriya, inda suka halaka mutane bakwai, suka kama 27, tare da kwato danyen mai da aka sace a wasu hare-haren da aka kai cikin sa’o’i 48 da suka gabata.
Wannan ci gaban ya biyo bayan umarnin da babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayar na ganin an kawar da duk wata ƙungiyar ta’addanci da masu laifi.
Ya kuma sake karfafa gwiwar dakarun rundunar yayin ziyararsa ta aiki zuwa yankin Arewa maso Gabas.



