Gwamnatin mulkin sojan Burkina Faso ta umurci masu gidajen mai na kasar da su saka kyamarorin tsaro daga yanzu, zuwa 1 ga watan sabuwar shekara mai kamawa ta 2026.
Umurnin na kunshe a cikin wata takarda da ministan tsaron kasar ya aike wa masu gidajen man.
Matakin ya biyo bayan wata ganawa ce da hukumomin kasar ta Burkina Faso suka yi da jagorori gidajen mai da dillalen man fetur na kasar wadanda suka dauki alkawalin ba da gudunmawar su domin yaki da ta’addanci a kasar.



