DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin inganta tsaro bayan rahoton Birtaniya

-

Gwamnatin Nijeriya ta ce tana daukar matakai don inganta tsaro a duk fadin Nijeriya biyo bayan sabon gargadi game da tafiye-tafiye da Birtaniya ta fitar kan jihohi da dama sakamakon ta’azzarar ayyukan ta’addanci, sace mutane tare da yin garkuwa da su.

Ofishin harkokin waje na Birtaniya ya ja hankalin ‘yan kasarsa da su guji dukkan tafiye-tafiye zuwa jihohin Borno, Yobe, Adamawa, Gombe, Katsina, da Zamfara, sannan ya yi gargadin kaucewa dukkan tafiye-tafiye sai dai idan ya zama dole.

Google search engine

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya ce gwamnati ta san da matsalolin tsaro kuma tana aiki tukuru wajen magance su, da kara inganta kayan aiki da ayyukan leken asiri, haka kuma dukkan baki a Nijeriya za su kasance cikin tsaro yayin da matakan ke ci-gaba da aiki.

Sai dai gwamnatin Jihar Gombe ta musanta gargadin, tana mai cewa bayanan da Birtaniya ta fitar basu dace ba kuma babu adalci a cikin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin kawo karshen yawaitar faduwar layin wutar lantarki

Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya karkashin Bola Ahmed Tinubu na aiki tukuru domin kawo karshen yawan faduwar layin wutar lanyarki...

Perez yana nan daram a Madrid – Fabrizio Romano

Shaharren dan jarida Fabrizio Romano ya bayyana cewa shugaban ƙungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Florentino Perez, bai da wani shirin barin kujerarsa duk da...

Mafi Shahara