DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar APC ta yaba wa Tinubu bisa tabbatar da adalci a zaben jihar Anambra

-

Jam’iyyar APC reshen jihar Legas ta yabawa shugaban Nijeriya Bola Tinubu bisa kare dimokuraɗiyyar Nijeriya ta hanyar guje wa tsoma baki a zaben gwamnan Anambra da aka gudanar a ranar Asabar.

Mai magana da yawun jam’iyyar a jihar, Mista Seye Oladejo, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, inda ya ce matsayar shugaban ta nuna jajircewarsa wajen tabbatar da sahihin zabe da kare dimokuraɗiyya.

Google search engine

Oladejo ya ce rashin tsoma bakin shugaban kasa a harkar zaben ya ƙara tabbatar da cancantarsa a matsayin gwarzon dimokuraɗiyya, tare da karfafa gwiwar jama’a a tsarin zabe.

Haka kuma, ya yabawa hukumar zabe ta INEC bisa gudanar da abin da ya kira zabe mai inganci da gaskiya, yana mai cewa jagorancin sabuwar hukumar ya kawo sabon salo na dimokuraɗiyya a Nijeriya.

A cewarsa, sakamakon zaben ya nuna rashin daidaito da tsari a cikin haɗakar jam’iyyun adawa, inda ya bayyana su a matsayin “taron ’yan siyasar da ke fafutuka da son zuciya ba tare da tsari ko hangen nesa ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara