Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya shawarci ’yan Nijeriya da sauran ’yan Afirka da aka soke musu biza a Amurka su gaggauta komawa gida kafin jami’an tsaron kasar su kama su.
A rubutunsa da ya wallafa a shafin X (Twitter) a ranar Litinin, Shehu Sani ya ce duk tsawon lokacin da mutum zai zauna a ƙasar waje, za a tuna masa wata rana cewa ba gidan mahaifinsa ba ne.
Wannan na zuwa ne bayan rahoton da ya nuna cewa gwamnatin Donald Trump ta soke fiye da biza 80,000 tun daga watan Janairun 2025, ciki har da bizar dalibai da wasu da ake zargi da laifukan ta’addanci da kuma karya dokoki kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ce sabbin matakan sun haɗa da rage wa’adin wasu nau’ikan biza ga ’yan Nijeriya da kuma buƙatar masu neman biza su buɗe asusunsu na sada zumunta domin ƙarin bincike a kansu.



