DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani mutum ya rasa ransa a wani gidan mata masu zaman kansu a jihar Rivers

-

Wani mutum da ba a tantance bayanansa ba ya rasa ransa bayan ya yanke jiki ya fadi a wani gidan mata masu zaman kansu da ke titin Azikiwe, Mile 2 Diobu, a Fatakwal, Jihar Rivers a ranar Lahadi.

Wasu majiyoyi sun ce mutumin ya yi sa-in-sa da guda daga cikin ma’aikatan gidan kafin ya fadi kasa inda aka garzaya da shi asibiti, likitoci kuma suka tabbatar da mutuwarsa.

Google search engine

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa an mika binciken ga sashen binciken manyan laifuka (SCID).

Rundunar ta kuma tabbatar da kama wani mutum da ake zargi da hannu a lamarin, yayin da wasu daga cikin matan da ke wurin suka arce bayan faruwar abin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara