DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan bindiga sun kai hari tare da sace mata 5 a kauyen ‘yan Kwada da ke jihar Kano

-

Wasu ’yan bindiga sun kai hari a kauyen ‘Yan Kwada da ke cikin kauyen Faruruwa, karamar hukumar Shanono a jihar Kano, inda suka sace mata biyar da suka haɗa da masu shayarwa a daren Lahadi.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa ’yan bindigar sun iso da yawansu dauke da makamai, inda suka kutsa gidaje da dama kafin su tafi da matan.

Google search engine

A cewarsa, daga cikin matan da aka sace, biyu sun dawo gida, yayin da uku har yanzu ke hannun ‘yan ta’addan.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa wannan harin ya faru ne mako guda bayan rundunar soji ta kashe ’yan bindiga 19 a fafatawar da suka yi a yankin.

Har ila yau, mazauna Faruruwa da sauran yankunan da ke kan iyakar Kano da Katsina na ci-gaba da rayuwa cikin fargaba sakamakon hare-hare ba kakkautawa, lamarin da ya tilasta wasu mazauna kauyukan yin ƙaura zuwa birane don tsira da rayuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara