DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An samu cacar baki tsakanin Wike da wani jami’in soja kan mallakar wani fili a Abuja

-

An samu musayar yawu a ranar Talata tsakanin ministan Abuja Nyesom Wike, da wani jami’in soja a yankin Gaduwa, Abuja, bayan takaddama kan iko da wani fili.

Bidiyon da aka gani ya nuna Wike yana zargin jami’in da mallakar filin ba bisa ka’ida ba, inda ya tambaye shi dalilin da ya sa sojoji ke iƙirarin mallakar filin a dalilin tsohon hafsan rundunar ruwan Nijeriya.

Google search engine

Jami’in, wanda ke sanye da kayan soji, ya ce an samu filin bisa doka kuma an bi dukkan ka’idojin da suka kamata, lamarin da ya fusata ministan har ya daka masa tsawa.

Har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, rundunar sojin Nijeriya ko hukumar FCTA basu fitar da wata sanarwa ba.

Hukumar FCTA ta Abuja dai na ci-gaba da kokarin hana kwace filaye da gina gine-gine ba bisa ka’ida ba a fadin birnin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara