DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Injiniya Sagir Koki ya fice daga jam’iyyar NNPP

-

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar birnin Kano a matakin tarayya Injiniya Sagir Ibrahim Koki, ya bayyana ficewarsa daga NNPP saboda rikicin cikin gida da ke kara kamari a cikin jam’iyyar.

A cikin wata wasika da ya rubuta ranar 11 ga Nuwamba, 2025, wacce ya tura wa shugabar jam’iyyar na mazabar Zaitawa, Koki ya ce ya dauki wannan mataki ne bisa tsarin dokar ƙasa da ke ba kowane ɗan Nijeriya ‘yancin shiga ko barin kowace jam’iyya.

Google search engine

Ya ce rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar a matakin kasa ya yi tsananin da har ya zama abin da ke hana shi gudanar da aikinsa yadda ya kamata da kuma wakiltar al’ummar Kano Municipal yadda ya kamata.

Hon. Koki, wanda aka zabe shi karkashin jam’iyyar NNPP a 2023, ya gode wa jam’iyyar bisa damar da ta bashi ya yi hidima ga al’umma, yana mai bayyana cewa goyon baya da amincewar da ya samu daga ‘ya’yan jam’iyyar sun kasance abin alfahari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu...

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Mafi Shahara