DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar PDP ta ce tana kan bakanta kan babban taron ta na kasa

-

Jam’iyyar adawa ta PDP a Nijeriya ta bayyana cewa ba za ta janye shirinta na gudanar da taron zaben shugabanninta na kasa da aka tsara a ranar 15 da 16 ga Nuwamba ba, duk da sabon umarnin kotun tarayya na hana yin taron.

Mataimakin mai magana da yawun jam’iyyar, Ibrahim Abdullahi, ya shaida wa Daily Trust cewa sabon hukuncin kotu bata lokaci ne kawai, yana mai cewa jam’iyyar na bin umarnin kotun koli wanda ya tabbatar da cewa jam’iyyu na da ikon gudanar da harkokinsu na cikin gida ba tare da tsoma bakin kotu ba.

Google search engine

Abdullahi ya ce PDP ba za ta lamunci abin da ya kira hukuncin da wasu suka tsara ba, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ta samu kafuwa daga ‘yan Nijeriya ne ba daga kotu ba.

A ranar Talata da ta gabata mai shari’a Peter Lifu na kotun tarayya da ke Abuja ya bayar da umarnin hana PDP gudanar da taron a Ibadan, tare da umartar INEC da kada ta sa ido ko ta amince da sakamakon taron, wanda ya biyo bayan karar da tsohon gwamnan Jigawa kuma dan takarar shugabancin jam’iyyar, Sule Lamido, ya shigar yana kalubalantar tsarin sayar da fom din takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu...

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Mafi Shahara