DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta katse zamanta na ranar Talata saboda muhawara kan kasafin kudin 2026

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta katse zamanta na ranar Talata sakamakon zazzafar muhawara kan kasafin kudin 2026

Jaridar Punch ta ruwaito cewa ba a samu gabatar da kuduri ko guda ba a zaman Talatar sakamakon daukar matakin, lamarin da ba a saba ganin irin sa ba.

Google search engine

Musayar yawu tsakanin ‘yan majalisar dai ya biyo bayan samun rabuwar kai game da yadda za a tafiyar da batun kasafin kudin Nijeriya na shekarar 2026.

Duk da cewa babu wata sanarwa a hukumance daga shugabancin majalisar, majiyoyi sun bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali ne kan wa’adin da aka bai wa ministocin kudi, kasafi da tsare-tsare tare da akanta janar na kasar, kan biyan basusukan da ‘yan kwangila ‘yan asalin Nijeriya ke bi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara