DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tattalin arzikin Nijeriya zai ninku zuwa shekarar 2037 — Ministar Kudi

-

Gwamnatin Nijeriya ta ce tana kan hanyar ninka tattalin arzikinta bisa ma’aunin GDP zuwa shekara ta 2037, bisa hadin gwiwar da ke tsakanin ma’aikatar kudi da babban bankin Nijeriya (CBN).

Karamar ministar kudi, Doris Uzoka-Anite ce ta bayyana haka a ranar Talata a Abuja yayin da take gabatar da jawabi a taron shekara-shekara na manyan jami’an babban bankin Nijeriya.

Google search engine

Ta ce samun hadin kai tsakanin bangarorin da suka shafi kudi na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasar.

A cewarta, burin gwamnati shi ne ta cimma karuwar GDP sama da kashi 4% a kowace shekara zuwa 2027, wanda hakan zai ninka darajar tattalin arzikin Nijeriya zuwa 2037 idan aka ci gaba da samun karuwar da ta kai kashi 7% a duk shekara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu...

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Mafi Shahara