DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dole mu karfafawa sojoji gwiwa saboda sadaukar da rayukansu da sukai – Tinubu

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya jinjina wa maza da mata na rundunar sojojin Nijeriya bisa jajircewa da sadaukarwar da suke yi don kare ƙasar daga barazanar tsaro.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa, Tinubu ya bayyana hakan ne a taron ƙungiyar Editocin Nijeriya NGE da aka gudanar a Abuja a ranar Laraba, inda ya ce sojojin suna fuskantar haɗari domin kare mutuncin kasar.

Google search engine

Shugaban ya ce duk da ƙalubalen da ake fuskanta na ta’addanci da ‘yan bindiga, gwamnatinsa tana ɗaukar matakai don karfafa rundunar sojoji da sauran jami’an tsaro.

A cewar sa, ya zama wajibi a ci gaba da kare su da kuma ba su goyon baya duba da irin hadarin da suke fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wadanda suka soke ni a baya yanzu yabo na suke – Olusegun Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo, ya ce ba za a taɓa gujewa suka ba a mulki, amma wadanda ke suka a yau su ne...

Bukola ya shawarci PDP da ta dakatar da babban taron ta na kasa

Tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya Bukola Saraki, ya shawarci jam’iyyar PDP ta dakatar da shirinta na gudanar da babban taronta na kasa da aka tsara...

Mafi Shahara