DCL Hausa Radio
Kaitsaye

NNPP ce za ta sake lashe zabe a jihar Kano – Shugabanta na Kasa Ajuji Ahmed

-

Shugaban jam’iyyar NNPP na Nijeriya Ajuji Ahmed, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta sake lashe zaben jihar Kano a 2027 duk da ficewar wasu ’yan majalisa daga cikinta.

Jaridar Punch ta rawaito Ajuji na cewa, rahotannin ficewar wasu mambobin majalisar wakilai daga jam’iyyar zuwa APC ba su rage damar da NNPP ke da shi ba, domin ficewar ta su jawo sababbin mambobi da dama suna shiga jam’iyyar musamman daga Kano.

Google search engine

Ficewar Abdulmumin Jibrin Kofa da Sagir Koki zuwa APC a ranar Alhamis ta biyo bayan karanta wasikunsu da kakakin Majalisar, Tajudeen Abbas ya yi, inda suka zargi rikicin cikin gida na jam’iyyar NNPP a Kano a matsayin dalilin ficewar.

Sai dai Ahmed ya ce NNPP ba ta damu ba, domin suna samun sababbin mambobi masu yawa, yana mai bayar da tabbatacin cewa NNPP za ta ci gaba da rike Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Na jagoranci yin sulhu da ‘yan bindiga akalla 600 – Sheikh Gumi

Sanannen Malamin addinin Musulunci Sheikh Ahmad Gumi ya mayar da martani ga masu kira da a kama shi kan tsokacinsa game da matsalar ‘yan bindiga...

Tinubu na shirin fitar da sunayen sabbin Jakadun Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu na shirin fitar da jerin sunayen jakadu da za su wakilci Nijeriya a manyan kasashe cikin makonni masu zuwa, a...

Mafi Shahara