Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan harin da aka kai Makarantar ‘yan mata ta Gwamnati da ke Maga a Jihar Kebbi, wanda ya yi sanadin mutuwar mataimakin shugaban makarantar da kuma sace wasu dalibai inda ya wannan al’amari ya sake tabbatar da irin tabarbarewar tsaron da ƙasar ke fuskanta.
A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na facebook, Atiku ya kuma yi Allah-wadai da kisan jigon APC, Umar Moriki, da kuma sace iyalai da dama a karamar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, yana mai bayyana wadannan hare-haren a matsayin aikata barna da ya sabawa duk wata al’umma mai bin doka.
Hakazalika, ya kuma ambaci irin tashin hankalin da ake fama da shi a Jihar Filato, Benue da wasu yankuna, inda ya ce al’ummomi na ci-gaba da fuskantar hare-hare.
Haka ma a karama Hukumar Shanono ta Kano, ya jaddada cewa mutanen yankin na tserewa daga gidajensu saboda fargabar hare-hare.
Madugun adawar ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta sake fasalin tsaro, ta ƙara yawan jami’an tsaro a yankunan da abin ya fi shafa tare da ƙara amfani da bayanan leƙen asiri wajen dakile hare-hare sannan kuma ya ce ’yan Najeriya sun cancanci kariya, mtuntawa da zaman lafiya.




Wannan maganar taka gaskiya ne Shugaban Kasarmu na Gobe da yardar Allah