DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro sun kaddamar da shirin ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

-

’Yan sanda da sojoji sun kaddamar da bincike da aikin ceto domin kubutar da dalibai 25 da aka sace daga makarantar ’Yan Mata ta gwamnati da ke Maga, ƙaramar hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A cewar rahotannin da aka samu daga jami’an tsaro, maharan sun kutsa makarantar da safiyar Litinin, inda suka hallaka ma’aikaci ɗaya tare da jikkata wani jami’in tsaro a lokacin da suka mamaye harabar makarantar.

Google search engine

Rundunar ’yan sanda ta tabbatar da lamarin, inda ta bayyana cewa tawagar da ke gadin makarantar ta yi musayar wuta da maharan, amma ’yan bindigar sun riga sun shiga cikin makarantar suka kwashe daliban zuwa wani wurin da ba a sani ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa an tura tawaga ta musamman tare da hadin gwiwar sojoji da sauran jami’an tsaro domin bin diddigin hanyoyin da maharan suka bi da kuma lalubo dazuzzukan da ake zargin sun tsere.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara