’Yan sanda da sojoji sun kaddamar da bincike da aikin ceto domin kubutar da dalibai 25 da aka sace daga makarantar ’Yan Mata ta gwamnati da ke Maga, ƙaramar hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A cewar rahotannin da aka samu daga jami’an tsaro, maharan sun kutsa makarantar da safiyar Litinin, inda suka hallaka ma’aikaci ɗaya tare da jikkata wani jami’in tsaro a lokacin da suka mamaye harabar makarantar.
Rundunar ’yan sanda ta tabbatar da lamarin, inda ta bayyana cewa tawagar da ke gadin makarantar ta yi musayar wuta da maharan, amma ’yan bindigar sun riga sun shiga cikin makarantar suka kwashe daliban zuwa wani wurin da ba a sani ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa an tura tawaga ta musamman tare da hadin gwiwar sojoji da sauran jami’an tsaro domin bin diddigin hanyoyin da maharan suka bi da kuma lalubo dazuzzukan da ake zargin sun tsere.




Ubangiji Allah ya Kubutar dasu, dama dukkan wadanda suke Hannun masu Garkuwa da Mutane