DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasashen Nijeriya, Mozambique da Sudan na daga cikin kasashen da ake musguna ma Kiristoci – Shugaban darikar Katolika

-

Jagoran Katolika, Pope Leo XIV, ya saka Najeriya cikin jerin kasashen da Kiristoci ke fuskantar tsangwama, tare da Bangladesh, Sudan, Mozambique, da wasu ƙasashe.

Leo ya wallafa hakan ne a shafinsa na X, inda ya nuna damuwarsa kan hare-haren da ake kaiwa al’ummomin Kiristoci da coci-coci, sannan ya yi kira da yin addu’o’i don zaman lafiya da hadin kai.

Google search engine

Maganganun Pope sun yi daidai da na shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya sanya Nijeriya a matsayin ‘kasar da ke cikin damuwa ta musamman’ kan tsangwamar addini ga Kiristoci wanda hakan ya jawo hankalin duniya kan batun tsangwamar addini a Nijeriya.

Sai dai gwamnatin Nijeriya ta musanta wannan zargi, tana mai cewa kasar ba ta nuna wariya ga wani addini ba, kuma tana matsayin kasa mai zaman lafiya da bin doka. Gwamnatin ta jaddada cewa matsalolin tsaro da ake fuskanta ba na addini ba ne, sai dai na laifuka daban-daban.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara