DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar Arewa maso Tsakiya ta jam’iyyar APC ta yi tir da zanga-zangar da wasu suka yi na nuna kin yarda da gwamnan Filato ya dawo APC

-

Kungiyar APC ta Arewa ta Tsakiya ta yi tir da zanga-zangar da wasu ‘yan APC na jihar Filato suka yi a Jos domin nuna kin amincewa da yiwuwar gwamna Caleb Mutfwang ya koma jam’iyyar inda ta bayyana wannan mataki a matsayin ba na dimokuradiyya ba ne, kuma babu wata doka da ta halatta shi.

A cewar shugaban kungiyar, Alhaji Saleh Zazzaga, babu wani mutum ko rukuni da ke da ikon hana kowane ɗan Najeriya shiga jam’iyyar da yake so, ciki har da gwamna mai mulki.

Google search engine

Zanga-zangar dai ta faru ne a yayin tarbar sababbin ‘yan jam’iyya da aka yi, inda wasu suka daga alluna suna nuna adawa da shigowar Mutfwang kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Kungiyar ta sake jaddada kiran da take yi wa Mutfwang ya sauya sheƙa zuwa APC domin ƙara wa jam’iyyar ƙarfi kafin 2027, tana zargin masu adawa da yunkurin da neman biyan bukatunsu na kai.

Punch ta ruwaito cewa kungiyar ta nemi Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamna Simon Lalong su shiga tsakani domin tabbatar da cewa an karɓi gwamnan cikin sauƙi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya nuna damuwarsa kan sace dalibai a jihar Kebbi

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan harin da aka kai Makarantar ‘yan mata ta Gwamnati da ke Maga a Jihar Kebbi,...

Jami’an tsaro sun kaddamar da shirin ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

’Yan sanda da sojoji sun kaddamar da bincike da aikin ceto domin kubutar da dalibai 25 da aka sace daga makarantar ’Yan Mata ta gwamnati...

Mafi Shahara