DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matatar man Dangote ta yi karin haske kan dalilin saukowar farashin man fetur

-

Matatar man Dangote ta bayyana rahotannin da ke cewa saukin farashin fetur ya samo asali ne daga dakatar da harajin shigo da fetur da dizal na kashi 15 a matsayin shaci-fadi.

Kamfanin ya ce gaskiyar lamarin shi ne saukin ya samo asali ne daga rage farashin wasu kayayyaki da kashi 5.6 a ranar 6 ga Nuwamba.

Google search engine

Dangote ya jaddada cewa harajin kaso 15 na shigo da kaya ya riga ya samu amincewar shugaban Nijeriya tun ranar 21 ga watan Oktoba, kuma hakan bai yi tasiri kan farashin kamfanin ba.

Hakazalika, ya tabbatar da ci-gaba da samar da fetur mai inganci a farashi mai rahusa, tare da kira ga kafofin watsa labarai da masu ruwa da tsaki su dogara kan sahihan bayanai wajen sanar da jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya nuna damuwarsa kan sace dalibai a jihar Kebbi

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan harin da aka kai Makarantar ‘yan mata ta Gwamnati da ke Maga a Jihar Kebbi,...

Jami’an tsaro sun kaddamar da shirin ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

’Yan sanda da sojoji sun kaddamar da bincike da aikin ceto domin kubutar da dalibai 25 da aka sace daga makarantar ’Yan Mata ta gwamnati...

Mafi Shahara