Zababben shugaban jam’iyyar PDP, Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ya ce jam’iyyar za ta yi la’akari da duk wani haɗin gwiwa da zai karfafa dimokuradiyya kafin zaben 2027.
Kabiru ya bayyana cewa PDP za ta mayar da hankali wajen ceto Nijeriya daga matsalolinta, sannan za ta bi kowace hanya ta siyasa wacce jama’a za su yaba da ita.
A cewarsa, jam’iyyar za ta yi aiki tare da sauran jam’iyyun adawa, kungiyoyin farar hula, da manema labarai domin tabbatar da dimokuradiyya, inda ya ce duk wani zaɓi da jama’a za su amince da shi za a yi la’akari da shi.



