DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya gargadi alkalan Nijeriya cewa adalci ba hajar sayarwa ba ce

-

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya gargadi alkalan Najeriya cewa dole adalci ya kasance a tsarkake ba tare da yunƙurin cakuda shi da rashawa ba.

Yayin taron alkalai da aka buɗe a Abuja a ranar Litinin, Tinubu ya ce alkalan manyan kotuna su ne ginshikan adalci, kuma gwamnati za ta ci gaba da zuba jari a horo, jin daɗi da aikin cibiyar shari’a ta ƙasa.

Google search engine

Tinubu ya jaddada cewa babu wani gyara da za ya yi tasiri ba tare da gaskiya da rikon amana ba, yana gargadin cewa cin hanci a bangaren shari’a na iya rushe ƙasar baki ɗaya.

Ya kuma nuna damuwa kan yawan shari’o’in da ke taruwa da jinkirin yanke hukunci, yana mai cewa dole kotuna su ɗauki matakai na gaggawa domin dawo da amincewar jama’a da ƙarfafa tsarin mulkin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya nuna damuwarsa kan sace dalibai a jihar Kebbi

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana damuwa kan harin da aka kai Makarantar ‘yan mata ta Gwamnati da ke Maga a Jihar Kebbi,...

Jami’an tsaro sun kaddamar da shirin ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

’Yan sanda da sojoji sun kaddamar da bincike da aikin ceto domin kubutar da dalibai 25 da aka sace daga makarantar ’Yan Mata ta gwamnati...

Mafi Shahara