DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babban hafsan sojin kasa ya umurci sojoji da su tsaurara wajen ganin sun ceto dalibai mata da aka sace a jihar Kebbi

-

Babban hafsan rundunar sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun Operation Fansan Yamma da su matsa kaimi wajen ceto daliban GGCSS Maga da aka yi garkuwa da su a Danko/Wasagu.

A cikin wata sanarwa da Kyaftin David Adewusi ta bayyana, Janar Shaibu ya umurci haka ne yayin kai ziyarar aiki a jihar Kebbi inda ya bukaci dakarun su yi aiki bisa bayanan leƙen asiri tare da bin sawun ’yan bindiga dare da rana, sannan da hada kai da ’yan banga da mafarauta domin sanin hanyoyin yankin.

Google search engine

Haka kuma, ya kai ziyarar ta’aziyya ga sarkin Danko da shugabar makarantar, yana tabbatar musu da cewa rundunar soji za ta tabbatar an kubutar da daliban ba tare da lahani ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ya umarci dakaru su kasance masu ladabi da ƙwarewa tare da bin ka’idojin aiki domin dawo da zaman lafiya a Kebbi da yankunan da ke makwabtaka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara