Sunday, March 22, 2026
HomeLabaraiDan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore ya yi Allah-wadai da sace dalibai...

Dan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore ya yi Allah-wadai da sace dalibai a jihar Kebbi

Dan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya yi Allah-wadai da sace ‘yan mata 25 daga Makarantar sakandare ta gwamnati, da ke a Maga, a karamar hukumar Danko-Wasagu ta jihar Kebbi, tare da kiran addu’a ga wadanda abin ya shafa.

Moore ya ce duk da har yanzu ba su samu cikakken bayani ba kan wannan mummunan hari, amma ya bayyana cewa yana kyautata zaton ya faru ne a wani yanki na Kiristoci a Arewacin Nijeriya, kuma ya bukaci hukumomi su dauki kwakkwaran mataki.

Google search engine

An kai harin ne da safiyar ranar Litinin, inda ‘yan bindiga suka shiga makarantar da makamai, suka hallaka mataimakin shugaban makarantar, tare da raunata wasu ma’aikata, sannan suka sace ‘yan mata 25 kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata