DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano za ta karfafa tsaro a iyakokin jihar

-

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya gana da kwamandojin rundunar ‘yan sanda don duba dabarun tsaro da karfafa matakan tabbatar da zaman lafiya a fadin jihar.

Taron, da aka gudanar a ranar Litinin a hedkwatar ‘yan sandan ta jihar Kano, ya hada manyan jami’an sassa daban-daban na ayukka da dabaru da leken asiri kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Google search engine

CP Bakori ya ce taron ya bai wa rundunar damar nazarin nasarorin da aka samu wajen hana laifuka da aiwatar da doka a jihar, tare da tsara hanyoyin kara karfafa ayyukan tsaro, kuma ya jaddada muhimmancin hada kai da al’umma, inda ya umarci shugabannin ayyukan da su karfafa wayar da kan jama’a a matakai na gida.

Hakazalika, ya ce taron ya mai da hankali musamman kan yanayin tsaro a kan iyakokin Kano, musamman karamar hukumomi Shanono, Tsanyawa da Rogo, inda ya bayyana ci-gaban da ake yi wajen kara jami’ai da kayan aiki, tare da bukatar a ci gaba da lura da sabbin barazanar tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara