DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Taraba ya dage komawa APC saboda sace ‘yan makaranta a Kebbi

-

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas ya sanar da jinkirta komawarsa jam’iyyar APC sakamakon sace ‘yan makaranta da ‘yan bindiga suka yi a Kebbi.

 

Google search engine

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan, Kefas ya bayyana cewa gabatar da wani lamarin siyasa a daidai lokacin da kasa ke cikin irin wannan yanayi na sabon jimamin matsalar tsaro ba abu ne da ya dace ba.

 

Jaridar Punch ta ruwaito sakataren jam’iyyar APC na Nijeriya Felix Morka, na bayyana cewa an dage bikin tarbar gwamnan zuwa wani lokaci da za a sanar nan gaba.

 

A baya dai an tsara ficewar gwamna Kefas daga jam’iyyar hamayya ta PDP, tare da komawa APC mai mulkin Nijeriya a ranar Laraba 19 ga watan Nuwamban 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Amnesty International ta koka kan halin da jihar Katsina ke ciki kan batun tsaro

Kungiyar kare hakin bil’adama ta Amnesty International ta gargadi cewa hare-haren ’yan bindiga da ƙungiyoyin ta’addanci suna tura Jihar Katsina zuwa ga mummunan bala’in jin-kai,...

Gwamnatin Sokoto ta kammala aikin samar da lantarki na kashin kanta na N7bn

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kammala aikin gina tashar samar da wutar lantarki ta mai zaman kanta, kamar yadda Kwamishinan Makamashi, Alhaji Sanusi Danfulani, ya bayyana...

Mafi Shahara