DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Bauchi ta dakatar da wasu manyan ma’aikatan gwamnati a jihar

-

Hukumar Kula da Ma’aikatan Gwamnati ta Jihar Bauchi ta dauki matakin ladabtar da wasu manyan ma’aikata huɗu saboda gagarumin cin amanar aiki a yayin gudanar da ayyukansu.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Mista Saleh Umar, ya fitar wa manema labarai a Bauchi ranar Juma’a.

Google search engine

Umar ya ce wannan mataki da aka dauka yayin zaman majalisar hukumar, na daga cikin ƙoƙarin da ake yi domin tsaftace harkokin aikin gwamnati a jihar.

Ya bayyana sunayen ma’aikatan da abin ya shafa kamar haka: Garba Hussaini, Darakta (Ilimi) kuma tsohon Provost; Haruna Umar, Mataimakin Darakta (Gudanarwa da Harkokin Ma’aikata); Umar Yusuf, Babban Jami’in Gudanarwa – Bursar; da Mohammed Usman, – Cashier; dukkaninsu na aiki ne a Kwalejin Fasahar Kimiyyar Lafiya ta Bill and Melinda Gates da ke Karamar Hukumar Ningi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara