Bwaje, ƙauye ne na manoma da ke cikin mazabar Gurdi a Karamar Hukumar Abaji ta Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja.
A cewar basaraken gargajiya na yankin, Malam Aliyu Isah, al’ummar sun shafe fiye da shekaru 100 da kafuwa a Cesar rahoton jaridar Daily Trust.
Tun waɗancan shekaru zuwa yau, shugaban ya ce ba su taɓa jin kamshin wani aiki daga gwamnati ba, ko ta Abuja, ko kuma ta Karamar Hukumar Abaji.
A cewarsa, al’ummar ba su da makaranta, cibiyar lafiya, hanya ko rijiyar burtsatse da za su kira ta su, sai dai idan sun yi tafiya zuwa wasu ƙauyuka.
Har ma idan lokacin zabe ya yi, shugaban ya ce dole sai sun yi tafiya zuwa makwabtan ƙauyuka domin kada kuri’a, domin ma har rumfar zabe ba a tanadar musu ba.



