DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Amurka na aiki da ta Nijeriya domin kawo karshen musguna ma Kiristoci da ‘yan ta’adda ke yi a kasar – Sakataren tsaron Amurka

-

Gwamnatin Amurka ta ce gwamnatin shugaba Donald Trump na aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin kawo ƙarshen abin da ta kira zaluntar Kiristoci da ’yan tada kayar baya ke yi a kasar, kamar yadda sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana.

Hegseth ya bayyana haka ne a shafinsa na X da Facebook bayan ganawarsa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da tawagarsa a Amurka.

Google search engine

A cewar sakataren, sun tattauna kan tashin hankaulan da ke addabar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce gwamnatin Trump na kokari sosai don dakile hare-haren da ake danganta wa ’da ‘yan tada kayar baya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ribadu ya jagoranci tawaga mai ƙarfi zuwa Amurka domin tattaunawa kan zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda kuma kafin haka shugaba Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake kallon suna da matsalar tauye ’yancin addini.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara