DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Amurka na aiki da ta Nijeriya domin kawo karshen musguna ma Kiristoci da ‘yan ta’adda ke yi a kasar – Sakataren tsaron Amurka

-

Gwamnatin Amurka ta ce gwamnatin shugaba Donald Trump na aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin kawo ƙarshen abin da ta kira zaluntar Kiristoci da ’yan tada kayar baya ke yi a kasar, kamar yadda sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth ya bayyana.

Hegseth ya bayyana haka ne a shafinsa na X da Facebook bayan ganawarsa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, da tawagarsa a Amurka.

Google search engine

A cewar sakataren, sun tattauna kan tashin hankaulan da ke addabar Kiristoci a Nijeriya, inda ya ce gwamnatin Trump na kokari sosai don dakile hare-haren da ake danganta wa ’da ‘yan tada kayar baya.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ribadu ya jagoranci tawaga mai ƙarfi zuwa Amurka domin tattaunawa kan zargin zaluntar Kiristoci a Nijeriya, inda kuma kafin haka shugaba Trump ya sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake kallon suna da matsalar tauye ’yancin addini.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara