DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Adamawa ta rufe makarantun kwana na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar

-

Gwamnatin jihar Adamawa ta umarci dukkan makarantun sakandare masu kwana na gwamnati da masu zaman kansu da su daina kwana nan take, saboda barazanar tsaro da ta kai ga sace dalibai a jihohin Neja da Kebbi.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, kwamishinan ilimi na jihar, Dr Umar Pella ya ce Gwamna Ahmadu Fintiri ya dauki matakin ne domin kare rayuwar dalibai.

Google search engine

Sanarwar ta bayyana cewa makarantun kwana sun zama babban wurin da ’yan ta’adda ke kai hari, don haka dukkan makarantu za su koma tsarin jeka-ka-dawo ba tare da bata lokaci ba. An umarci dukkan shugabannin makarantu da masu makarantu su aiwatar da wannan sauyi cikin gaggawa.

Hakan na faruwa ne a lokacin da jihohi da dama irin su Kwara, Filato, Katsina da Neja suka rufe makarantu saboda tashin hankali, yayin da Taraba ma ta umurci daina kwana. A lokaci guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara