DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kebbi ta bukaci addu’o’i daga al’umma domin dawo da daliban da aka sace cikin aminci

-

Gwamnatin jihar Kebbi ta bukaci al’umma su tsananta addu’o’i domin ceto ɗaliban GGCSS Maga da ’yan ta’adda suka sace, kamar yadda kwamishinan harkokin addini, Sani Aliyu, ya bayyana a Birnin Kebbi.

jaridar Punch ta ruwaito kwamishinan ya ce halin da ake ciki ya zarce ƙarfin ɗan adam, don haka ana buƙatar cikakken taimakon Allah duk da ƙoƙarin gwamnati da jami’an tsaro.

Google search engine

Aliyu ya roƙi malamai, limamai, da masu ibada su rika yin qunut da addu’o’i a cikin sallolinsu, musamman a cikin dare. Haka kuma ya bukaci fastoci da su ware lokuta a cikin wa’azozinsu da taron ibada domin roƙon zaman lafiya a Kebbi da Nijeriya gaba ɗaya.

Hakazalika, kwamishinan ya kuma yi kira ga jama’a su kasance masu lura, su nisanci hulɗa da miyagu, tare da tura duk wani muhimmin bayani ga jami’an tsaro domin taimakawa wajen gano masu laifi da kuma ceto ɗaliban cikin gaggawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara