DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Neja ta sanar da rufe daukacin makarantun firamare da sakandare na jihar

-

Gwamnatin Jihar Neja ta ce ta rufe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu na firamare da sakandare bayan sace daliban makarantar St. Mary’s Catholic da ke Papiri a Agwara.

Wannan na cikin sanarwar da aka fitar bayan taron tsaro da Gwamna Umar Bago ya yi da shugabannin hukumomin tsaro, kamar yadda mai magana da yawunsa, Bologi Ibrahim, ya bayyana.

Google search engine

Gwamnan ya ce makarantun boko, Islamiyoyi da kwalejojin tarayya ciki har da FGC Minna, duk sun shiga jerin makarantun da aka rufe, sai dai matakin bai shafi manyan makarantu ba face waɗanda ke yankunan da aka ayyana masu hadari a Neja ta Arewa da Gabas.

Bago ya kuma jaddada cewa gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro wajen ceto daliban, inda ake ci-gaba da lissafi domin tantance adadin waɗanda aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara