DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Neja ta sanar da rufe daukacin makarantun firamare da sakandare na jihar

-

Gwamnatin Jihar Neja ta ce ta rufe dukkan makarantun gwamnati da masu zaman kansu na firamare da sakandare bayan sace daliban makarantar St. Mary’s Catholic da ke Papiri a Agwara.

Wannan na cikin sanarwar da aka fitar bayan taron tsaro da Gwamna Umar Bago ya yi da shugabannin hukumomin tsaro, kamar yadda mai magana da yawunsa, Bologi Ibrahim, ya bayyana.

Google search engine

Gwamnan ya ce makarantun boko, Islamiyoyi da kwalejojin tarayya ciki har da FGC Minna, duk sun shiga jerin makarantun da aka rufe, sai dai matakin bai shafi manyan makarantu ba face waɗanda ke yankunan da aka ayyana masu hadari a Neja ta Arewa da Gabas.

Bago ya kuma jaddada cewa gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro wajen ceto daliban, inda ake ci-gaba da lissafi domin tantance adadin waɗanda aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara