DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Taraba ta umurci rufe makarantun kwana a fadin jihar

-

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya umarci duk makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu da dalibai su daina kwana a makarantu da dalibai saboda fargabar tsaro a faɗin ƙasar.

Sanarwar hakan ta fito ne daga kwamishinar ilimi ta jihar, Dr Augustina Godwin, wadda ta ce garkuwa da ɗalibai a Kebbi da Neja ta sanya daliban makarantun kwana zama cikin hadari, don haka gwamnati ta umarci komawa tsarin jeka-ka-dawo har sai tsaro ya inganta kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Umarnin ya zo ne a rana guda bayan ’yan ta’adda sun sace dalibai daga makarantar St. Mary a Papiri, Neja, yayin da kusan mako guda da aka yi garkuwa da dalibai 25 a Maga, jihar Kebbi. Lamarin da ya ƙara nuna tabarbarewar tsaro a makarantun Arewacin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara