DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dinkin duniya ta yi Allah-wadai da sace dalibai a jihar Neja

-

Majalisar dinkin duniya ta yi kakkausar suka kan sace ɗalibai da malamai daga makarantar St. Mary’s a Papiri, jihar Neja, inda ta ce harin abin takaici ne kuma makarantu wajibi ne su kasance wuraren kariya ga ɗalibai.

A cewar kungiyar Kiristocin Nijeriya, CAN, ’yan bindigar sun sace ɗalibai 215 da malamai 12, lamarin da ya zo kwanaki bayan sace ɗalibai 25 da kashe malami a Maga, da ke jihar Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

MDD ta ce dole a mai da hankali kan ganin an dawo da yaran cikin gaggawa, ta kuma jaddada bukatar aiwatar da yarjejeniyar kariyar makarantu, yayin da gwamnatin Nijeriya ta rufe makarantun Unity 41 domin guje wa sake faruwar irin wadannan hare-haren.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara