DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Trump na Amurka ya sake aibata Nijeriya inda ya zargi gwamnati da gazawa a harkar tsaro

-

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake sukar Nijeriya, inda ya kira ta da “abin kunya” tare da zargin gwamnati da kasa dakile kashe-kashen da ake yi wa ’yan ƙasa. Ya ce ana kashe mutane dubbai ba tare da wani mataki ba, inda ya zargi gwamnati da gazawa.

Kalaman Trump sun zo ne bayan ya sake saka Nijeriya a jerin ƙasashen da ake kula da su na musamman, yayin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta tura mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, zuwa Amurka don gabatar da bayanai kan matakan tsaro.

Google search engine

Tun bayan kalaman Trump, hare-haren sun ƙaru a yankuna daban-daban inda ‘yan bindiga suka halaka babban hafsan soja a Borno, yayin da barayin daji suka sace dalibai mata 25 a Kebbi tare da halaka mataimakin shugaban makarantar.

A ciki ƙarin hare-haren, ’yan bindiga sun kutsa coci a Eruku, Kwara, sannan suka sace fiye da ɗalibai 300 da malamai 12 daga makarantar St Mary’s a Papiri, Jihar Neja, abin da ya kara nuna tsananin tabarbarewar tsaro a ƙasar kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara