DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dalibai 50 cikin daliban jihar Neja da aka sace sun tsere daga hannun masu garkuwa da mutane – Kungiyar CAN

-

Dalibai 50 daga cikin waɗanda aka sace a makarantar St. Mary’s Secondary and Primary School da ke Papiri a ƙaramar hukumar Agwara ta jihar Neja sun tsere daga hannun ’yan bindiga kuma sun koma gidajensu lafiya.

A cewar shugaban Kungiyar Kiristoci Nijeriya reshen jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ne mamallakin makarantar, waɗannan daliban sun kuɓuta ne a ranar Asabar kuma aka haɗa su da iyalansu, kamar yadda sanarwar sakatariyarsa ta bayyana a ranar Lahadi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Google search engine

Rev. Yohanna ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a aji na firamare, inda 377 suke na kwana. Ya ce yanzu haka, bayan waɗanda suka tsere, dalibai 236, 14 na sakandare da ma’aikata 12 na nan a hannun ’yan bindiga, yayin da hukumomin tsaro ke ƙoƙarin ceto su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara