DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Firaministar Italiya ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta kare rayukan Kiristoci a kasar

-

Fira-ministar kasar Italiya, Giorgia Meloni, ta bukaci gwamnatin Nijeriya ta kara tsaurara matakan tsaro domin kare Kiristoci a sassa daban-daban na Nijeriya.

A wata sanarwa da ta wallafa a X a ranar Juma’a, Meloni ta bayyana harin da aka kai wa al’ummomin Kirista a Nijeriya a matsayin mummuna kuma abin ƙyama. Ta bukaci hukumomi su dauki matakin gaggawa domin hukunta masu aikata irin wadannan laifuka.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Meloni ta ce ’yancin yin addini hakki ne da ba ya karyewa, tana mai jaddada cewa dole ne gwamnati ta kare dukkan rukunan addinai ba tare da wariya ba.

Haka kuma ta nuna alhini ga iyalan da lamarin ya shafa da al’ummomin da ke fargaba sakamakon hare-haren da ake kai musu.

Wannan furuci ya fito ne a lokacin da ake cikin damuwa kan yadda hare-haren ’yan bindiga, ’yan ta’adda ke kamari kan al’umma a Nijeriya, tare da sace-sace da kai farmaki ga kauyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara