Gwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkan makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar saboda karuwar barazanar tsaro.
Hakan ya shafi manyan makarantu na jihar, ban da kwalejin koyon jinya ta Birnin Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A cikin sanarwar da kwamishinonin ilimi Halima Bande da Isa Abubakar-Tunga suka fitar, gwamnati ta ce matakin kariya ne bayan hare-hare da garkuwa da ’yan mata a Maga inda suka ce dole ne a tabbatar da lafiyar dalibai da ma’aikata a yanzu.
Matakin ya shafi daruruwan makarantu a kananan hukumomi 21, yayin da iyaye da dama ke cikin fargaba saboda hare-haren da suka auku kwanakin baya.
Abubakar-Tunga ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar tsaro kuma za a sanar da sabon ranar dawowa idan yanayi ya inganta.



