DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkanin makarantun gwamnati da masu zaman kansu saboda barazanar tsaro a jihar

-

Gwamnatin jihar Kebbi ta rufe dukkan makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu a fadin jihar saboda karuwar barazanar tsaro.

Hakan ya shafi manyan makarantu na jihar, ban da kwalejin koyon jinya ta Birnin Kebbi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

A cikin sanarwar da kwamishinonin ilimi Halima Bande da Isa Abubakar-Tunga suka fitar, gwamnati ta ce matakin kariya ne bayan hare-hare da garkuwa da ’yan mata a Maga inda suka ce dole ne a tabbatar da lafiyar dalibai da ma’aikata a yanzu.

Matakin ya shafi daruruwan makarantu a kananan hukumomi 21, yayin da iyaye da dama ke cikin fargaba saboda hare-haren da suka auku kwanakin baya.

Abubakar-Tunga ya ce an ɗauki matakin ne bisa shawarar tsaro kuma za a sanar da sabon ranar dawowa idan yanayi ya inganta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara