DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kare kai da wasu garuruwan ke yi na kara haddasa matsaloli maimakon magance su a jihar Filato – Rundunar sojin Nijeriya

-

Rundunar Sojin Najeriya ta ce barin al’ummomi su kare kansu daga maƙiya ba ya magance rikice-rikicen da faruwa a jihar Filato, illa ƙara tsananta su.

Babban daraktan hulɗar sojoji da fararen hula, Manjo Janar MA Etsy-Ndagi, ya bayyana haka ne a Jos, yana mai cewa tsarin bai taba haifar da da mai ido ba.

Google search engine

A cewarsa, rikicin manoma da makiyaya ya koma salo na hare-hare da ramuwar gayya, inda kowane ɓangare ke zargin ɗaya da farauta ko lalata dukiya.

Hakazalika ya ce dole ne a kwace dukkan makamai kowane iri domin a sami zaman lafiya mai ɗorewa kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Etsy-Ndagi ya jaddada cewa sojoji ba sa goyon bayan al’ummomi su ɗauki doka a hannunsu, sai dai suna kare garuruwan da ke fuskantar tashin hankali. Ya kuma yi kira ga mazauna Filato da su zauna lafiya su kuma ba ƙungiyoyin tsaro hadin kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara