DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

-

Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa.

An dai ware kujerar shugaban APC na ƙasa ga Arewa ta Tsakiyar Nijeriya a taron jam’iyyar na 2022, abin da ya haifar da fitowar tsohon Gwamnan Nasarawa, Adamu Abdullahi. Amma bayan murabus ɗinsa a 2023 ba tare da kammala wa’adin ba, sai aka naɗa Abdullahi Ganduje, tsohon Gwamnan Kano daga Arewa maso Yamma, a matsayin shugaban jam’iyyar.

Google search engine

Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC a Arewa ta Tsakiyar Nijeriya wadda ta ƙunshi manyan jiga-jigan jam’iyyar daga jihohin yankin, ta yi zanga-zanga, tarurruka, taron manema labarai da bayanai domin ganin an mayar da kujerar ga yankin. A ƙarshe, a ranar 24 ga Yuli, 2025, aka naɗa Farfesa Nentawe Yilwatda daga Jihar Filato a matsayin shugaban jam’iyyar.

Sai dai yanzu kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC Forum ta ce Yilwatda ya gaza nuna ƙwarewar jagoranci.

Kungiyar ta bayyana haka ne cikin wata sanarwa da Shugabanta, Alhaji Saleh Zazzaga, ya fitar a Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Zargin El-Rufa’i na biyan ‘yan bindiga Naira biliyan daya ba gaskiya ba ne – Gwamnatin Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta musanta zargin da tsohon gwamna jihar, Nasir El-Rufa’i ya yi a Channels TV cewa gwamnatin Uba Sani ta biya ’yan bindiga...

Mafi Shahara