DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya sun kama wani da ake zargi da satar mutane inda yake neman kudin fansa Naira miliyan 20 a jihar Taraba

-

Sojojin birget na 6 na rundunar sojin Nijeriya sun kama wani da ake zargi da satar mutane mai suna Umar Musa Geyi, a Wukari da ke jihar Taraba a ranar 22 ga watan Nuwamba 2025, yayin da ake zargin yana neman kudin fansa na Naira miliyan 20 daga iyalan wanda aka sace.

Ana zargin wanda aka kama yana da hannu a sace Alhaji Jano, wani Bafulatani mazaunin Jandei–Kulala, wanda aka sace a ranar 13 ga watan Nuwamba, kuma har yanzu yana hannun wadanda suka yi garkuwa da shi.

Google search engine

Kwamandan birget na 6, Birgediya-Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin kan kwarewarsu, inda ya jaddada kudurin rundunar na karyawa da kawar da dukkan hanyoyin aikata laifuka a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara