DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya sun kama wani da ake zargi da satar mutane inda yake neman kudin fansa Naira miliyan 20 a jihar Taraba

-

Sojojin birget na 6 na rundunar sojin Nijeriya sun kama wani da ake zargi da satar mutane mai suna Umar Musa Geyi, a Wukari da ke jihar Taraba a ranar 22 ga watan Nuwamba 2025, yayin da ake zargin yana neman kudin fansa na Naira miliyan 20 daga iyalan wanda aka sace.

Ana zargin wanda aka kama yana da hannu a sace Alhaji Jano, wani Bafulatani mazaunin Jandei–Kulala, wanda aka sace a ranar 13 ga watan Nuwamba, kuma har yanzu yana hannun wadanda suka yi garkuwa da shi.

Google search engine

Kwamandan birget na 6, Birgediya-Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa sojojin kan kwarewarsu, inda ya jaddada kudurin rundunar na karyawa da kawar da dukkan hanyoyin aikata laifuka a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara