Kungiyar mabiya addinin kirista ta Nijeriya ta bayyana cewa wani mahaifi ga dalibai uku cikin wadanda aka sace a Neja ya rasu sakamakon ciwon zuciya.
Shugaban kungiyar na arewacin Nijeriya da kuma Abuja Rev. John Hayab shi ne ya bayyana hakan a tattaunawar sa da gidan talabijin na Arise.
John Hayab ya ce mahaifin yaran mai suna Mr. Anthony, ya kadu matuka da samun labarin sace ‘ya’yan nasa, dalili kenan da ya haddasa masa bugun zuciya.
Ya nuna damuwa da irin halin tashin hankali da iyayen yaran da aka sace a makon da ya gabata suka tsinci kawunan su, musamman a jihohin Kebbi, Kwara da Neja.
Sai da har zuwa wannan lokaci jaridar Punch ba ta tabbatar da sahihancin iƙirarin mutuwar mahaifin a sanadiyyar bugun zuciyar ba.



