DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mahaifin dalibai uku da aka sace a Neja ya rasu – Kungiyar CAN

-

Kungiyar mabiya addinin kirista ta Nijeriya ta bayyana cewa wani mahaifi ga dalibai uku cikin wadanda aka sace a Neja ya rasu sakamakon ciwon zuciya.

 

Google search engine

Shugaban kungiyar na arewacin Nijeriya da kuma Abuja Rev. John Hayab shi ne ya bayyana hakan a tattaunawar sa da gidan talabijin na Arise.

 

John Hayab ya ce mahaifin yaran mai suna Mr. Anthony, ya kadu matuka da samun labarin sace ‘ya’yan nasa, dalili kenan da ya haddasa masa bugun zuciya.

 

Ya nuna damuwa da irin halin tashin hankali da iyayen yaran da aka sace a makon da ya gabata suka tsinci kawunan su, musamman a jihohin Kebbi, Kwara da Neja.

 

Sai da har zuwa wannan lokaci jaridar Punch ba ta tabbatar da sahihancin iƙirarin mutuwar mahaifin a sanadiyyar bugun zuciyar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara