DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojojin Nijeriya sun kama wadanda ake zargi da satar mutane 56 tare da ceto 45 cikin mako ɗaya

-

Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarunta sun halaka ’yan ta’adda da dama, sun kama mutane 57 da ake zargi, tare da ceto mutane 45 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda, a cewar daraktan yaɗa labaran tsaro, Manjo-Janar Michael Onoja.

A cewarsa, dakarun sun kuma kwato makamai, motoci da harsasai, tare da rusa sansanonin ’yan ta’adda a yankuna daban-daban kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

A Arewa maso Gabas, Operation Hadin Kai ta kashe ’yan ta’adda da dama, ta kama mutane 11 da ake zargi da taimaka musu, ta kuma kubutar da fasinjoji 8 da aka sace. Jiragen yakin sama sun yi luguden wuta a dajin Sambisa, inda suka halaka ’yan ta’adda tare da lalata wuraren boye makamansu.

Haka kuma, dakarun Operation FASAN YAMMA, sun hallaka ’yan bindiga da dama, tare da kama 15, da kuma ceto mutane 13 a jihohin Zamfara, Kebbi, Sokoto, Katsina, Kaduna da Neja. Dakarun sun kuma kwato makamai, motocci, dabbobi da kuma wani dillalin makamai dauke da Naira miliyan 4 da makamai irin na soji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara