DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana zargin ‘yan bindiga da sace budurwa sa’o’i kadan kafin daurin aurenta a jihar Sokoto

-

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kutsa kauyen Chacho a karamar hukumar Wurno ta jihar Sokoto da tsakar dare, inda suka yi awon gaba da amarya da kawayenta sa’o’i kaɗan kafin a daura aurenta.

Lamarin, wanda ya faru misalin ƙarfe 1 da rabi daren Lahadi, ya shafi amarya, kawaye, tare da wasu bakwai mata da mutum ɗaya namiji da aka ce an yi garkuwa da su, yayin da mutum ɗaya ya jikkata.

Google search engine

Mazauna kauyen sun koka kan jinkirin zuwan jami’an tsaro, inda suka ce an sanar da su tun da wuri amma suka iso bayan awa guda kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kakakin rundunar ’yan sandan Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa har yanzu cikakkun bayanai ba su fito ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara