Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kutsa kauyen Chacho a karamar hukumar Wurno ta jihar Sokoto da tsakar dare, inda suka yi awon gaba da amarya da kawayenta sa’o’i kaɗan kafin a daura aurenta.
Lamarin, wanda ya faru misalin ƙarfe 1 da rabi daren Lahadi, ya shafi amarya, kawaye, tare da wasu bakwai mata da mutum ɗaya namiji da aka ce an yi garkuwa da su, yayin da mutum ɗaya ya jikkata.
Mazauna kauyen sun koka kan jinkirin zuwan jami’an tsaro, inda suka ce an sanar da su tun da wuri amma suka iso bayan awa guda kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Kakakin rundunar ’yan sandan Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa har yanzu cikakkun bayanai ba su fito ba.



