DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Kebbi ya gana da shugaba Tinubu bayan ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

-

Shugaba Bola Tinubu ya karɓi Gwamnan Kebbi, Nasir Idris, a fadar shugaban Nijeriya Abuja, inda suka tattauna kan ayyukan tsaro a Arewa maso Yamma da ceto ɗalibai ’yan makarantar GGCSS Maga da aka sace a ranar 17 ga watan Nuwamba.

Gwamnan ya gode wa Shugaba Tinubu bisa umarnin gaggawa da kuma yadda hukumomin tsaro da leƙen asiri na tarayya suka samu nasarar ceto ɗaliban a ranar 26 ga watan Nuwamba, kafin a miƙa su ga iyayensu a Birnin Kebbi. Ya kuma yaba wa ministan tsaro, Bello Matawalle, bisa jagorantar aikin ceton.

Google search engine

Taron ya zo ne a lokacin da ake fama da sake ƙaruwa da garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, musamman hare-haren da ke nufi a makarantu kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara