DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar ADC tsagin Atiku na duba yiwuwar daukar Peter Obi ko Amaechi a matsayin ‘yan takarar mataimakin shugaban kasa a zaben 2027

-

Jam’iyyar ADC bangaren Atiku Abubakar ya fara neman ɗan takarar mataimaki daga Kudu domin zaben 2027, inda ake duba yiwuwar daukar tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Labour Party, Peter Obi. Idan Obi ya ƙi amincewa, ana sa ran Atiku zai koma ga tsohon gwamnan Rivers, Rotimi Amaechi.

Dele Momodu, abokin siyasar Atiku, ya ce haɗin gwiwar Atiku da Obi ita ce mafi ƙarfi wajen kalubalantar shugaba Bola Tinubu, yana tunasar da cewa sun taba yin tikitin tare a 2019 kafin su yi takara dabam a 2023.

Google search engine

Momodu ya dora laifin rashin haɗin kan su kan wasu magoya bayan Obi, yana mai cewa babu ’yan siyasa daga Kudu kaɗai da za su iya kayar da Tinubu. Ya ce tuni ya sha yi wa Obi magana cewa ya yi gaggawar rungumar wannan dama ko kuma Atiku ya koma ga Amaechi, wanda ya ce yana da ƙwarewar siyasa sosai.

Hakazalika, ya gargadi Obi cewa jinkiri na iya jawo masa rasa babbar dama a 2027, yana mai cewa Atiku bai da lokaci wajen jira kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara