DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar Miyetti Allah ta yi alkawarin aiki hannu da hannu da jami’an tsaro a jihar Kaduna

-

Kungiyar Miyetti Allah (MACBAN) reshen Kudancin Kaduna ta bayyana aniyar haɗa kai da hukumomin tsaro domin magance matsalar tsaro a yankin.

Wannan kudiri ya fito ne a taron da aka gudanar a Kafanchan, hedkwatar karamar hukumar Jema’a, a ranar Lahadi.

Google search engine

Shugaban MACBAN na yankin Kudancin Kaduna, Alhaji Mato Yahaya, ya ce lokaci ya yi da za a nemo mafita, tare da yin kira ga shugabanni su faɗi gaskiya kuma su gabatar da shawarwari masu amfani domin magance matsalolin yankin. Ya kuma jaddada muhimmancin zaman lafiya tsakanin makiyaya da sauran al’umma.

A nasa jawabin, shugaban MACBAN na jihar Kaduna, Alhaji Abdulhamid Albarka, ya ce an shirya taron ne domin tattara ra’ayoyin jagororin Fulani na ƙananun hukumomi, sannan a mika su ga hukumomin tsaro domin ɗaukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara