Wasu ’yan bindiga sun tare motoci a kan hanyar Isanlu–Makutu–Idofin da ke Yagba ta Gabas a jihar Kogi, inda suka yi garkuwa da matafiya da dama.
Mazauna wajen sun ce maharan sun kafa shinge na tsawon sa’o’i, inda motoci uku suka faɗa tarkonsu, kuma mutum ɗaya kacal ya kuɓuta.
Kamar yadda mazauna yankin suka shaida, jami’an soji da ’yan sa-kai sun bi sawun maharan daga baya suka kuma yi musayar wuta da su, lamarin da ya kai ga kubutar da wasu daga cikin fasinjojin da aka sace.
Kakakin ’yan sandan jihar, CSP William Aya, ya ce mutum biyu aka sace yayin da wani Raji Adesukami ya tsere, kuma an tura tawaga ta musamman domin ceto sauran.
Wata majiya ta rundunar soji ta bayyana cewa sojojin Birget ta 12 sun ceto mutane biyar a yayin wani samame da suka kai a yankin Isanlu–Egbe a ranar 29 ga Nuwamba, bayan wasu hare-haren sace mutane da suka afku a yankin.
A halin yanzu, Gwamna Usman Ododo ya ce za a kai farmaki kai tsaye cikin dazukan da ’yan bindiga ke ɓoyewa domin kare rayukan jama’ar jihar kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.



