DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnati na daf da fallasa masu ingiza ta’addanci a Nijeriya – Daniel Bwala

-

Hadimin shugaba Tinubu na Nijeriya Daniel Bwala ya bayyana cewa gwamnati na daf da kwarmata sunayen masu daukar nauyin ta’addanci a kasar.

Bwala ya bayyana haka ne yayin hira da ‘Television Continental’ a ranar Lahadi, yana mai bayyana cewa tuni gwamnatin Tinubu ta fara daukar tsauraran matakai kan lamuran tsaro a kasar, wadanda za su bayyana ga ‘yan Nijeriya nan ba da jimawa ba.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Hadimin shugaban na cewa gwamnatin ta kusa fallasa sunayen masu daukar nauyin duk wani nau’i na tashin hankali da ake fama da shi a sassan kasar.

Kazalika ya jaddada bukatar samar da hadin kai a tsakanin kasashe musamman masu makwabtaka da juna wajen yakar matsalar tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara